👇👇👇
#Assalamu__alaikum__everyone
#DUNIYA_MAKARANTA
#RAMDAN_PROGRAM_DAY_FIVE🌙
#TIME_ 8:30Am to 90:00pm,
ME KE HALATTA GA MAI AZUMI
• Haƙiƙa ALLAH TA'ALAH yayi wa Musulmi sauƙi lokacin Azumi da daddare su sadu da iyalansu.
ALLAH TA'ALAH yace:
An halatta gareku a daren Azumi ku kusanci matanku.
[Suratul Bakara: aya ta 187]
Ma'ana bayan ansha ruwa, ya halatta namiji yayi kwanciyar aure da matarsa.
Barra’u yace: Yayin da ALLAH {S.W.T} ya wajabta Azumin Ramadan, sahabbai sun kasance basa saduwa da iyalansu da daddare, har sai da ALLAH ya saukar da wannan ayar.
• Babu laifi mai Azumi ya wayi gari da janaba a cikin watan Ramadan.
Nana Aisha da Ummu-Salama (R.A) suka ce:
Manzon ALLAH {s.a.w} ya kasance alfijir yana riskarsa yana mai janabar saduwa da iyalansa, sannan yayi wanka kuma yayi Azumi.
[Bukhari ne ya rawaito].
Nana Aisha (R.A) tace:
Manzon ALLAH {s.a.w} ya kasance yana runguma ta lokacin da yake Azumi kuma nima ina Azumi.
[Abu Dawud].
Ma'ana yakan rungume matarsa da rana alhalin yana cikin azumi.
Saboda haka dan mutum ya sumbaci matarsa koya rungume ta har ya fitar da maziyyi, to ba komai a gareshi, azuminsa yana nan.
Idan kuma mutum ya rungumi matarsa ko ya sumbace ta, lokacin duk suna Azumi har ɗayansu ya zubar da maniyyi, to Azumin wanda ya zubar da maniyyin ya ɓaci kuma sai ya rama Azumi.
• Yin Qaho: Idan mutum yana Azumi sai yasa akayi masa ƙaho, shima ba komai a gareshi.
Daga Ɗan Abbas (R.A) yace:
Manzon ALLAH {s.a.w} yayi ƙaho a lokacin da yake Azumi.
HUKUNCIN MAI AZUMIN DA YACI ABINCI DA MANTUWA
Idan mutum yana Azumi sai yaci ko ya sha abin sha da mantuwa, azuminsa ingantacce ne, babu ramuwa a gareshi bare kaffara.
Abu Huraira (R.A) yace:
Manzon ALLAH {s.a.w} yace:
Wanda ya manta yaci ko ya sha lokacin da yake Azumi, to yaci gaba da azuminsa, hakiƙa, ALLAH ne yaci da shi ya shayar dashi.
[Bukhari ne ya rawait

Comments
Post a Comment